Rundunar ƴan sanda shiyya ta daya Zone One, dake jihar Kano, ƙarƙashin AIG Umar Mamman Sanda ta gurfanar da jarumar Kannywood Amal Umar a gaban kotun majistiri mai lamba 24 dake unguwar gyadi-gyadi a birnin Kano.
Wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yan sandan CSP Bashir Muhammad ya fitar, ta ce an gurfanar da Amal Umar a gaban kotun ne bisa zargin ta da yunƙurin bawa wani ‘dansanda cin-hancin kuɗi Naira Dubu Ɗari biyar.
Acewar binciken ‘yan sandan, Amal Umar ta fara ne da baiwa ɗan sandan da ke bincike a kan wani laifi da ake zarginta da hannun wajan aikatawa naira dubu dari biyu da hamsin (250,000).
0 Comments