CBN Ya Fitar Da Sanarwa Kan Wa'adin Karbar Tsoffin Takardun Kudade


Babban Bankin Najeriya, CBN ya bayyana cewa za a ci gaba da amfani da tsoffin kudade a kasar. 

Bankin ya bayyana haka ne ta bakin daraktan yada labarai, Isa AbdulMumin a yau Laraba 8 ga watan Nuwamba. 

Wannan na zuwa ne yayin da ake ci gaba da korafin karancin kudade a kasar, cewar Punch. 

Har ila yau, bankin ya musanta cewa akwai karancin kudin inda ya ce akwai makudan kudade da za su isa juya harkar kasuwanci. 

Sanarwar ta ce: 

"Saboda gudun kokwanto, mu na da isassun kudade da za a yi harkokin kasuwanci da su. 

"Mu na sanar da ku cewa duk wani kudi da aka ba ku halastacce ne, bai kamata ku ki karba ba." 

Bankin ya bai wa sauran bankuna umarnin ci gaba da bayar da sabbi da tsoffin kudade a kasar. 

Post a Comment

0 Comments